Kamfanin Dillancin Labaran Ƙasa Da Ƙasa Na Ahlul-Baiti (As) – Abna - ya bayar da rahoton cewa: Mataimakin gwamnan lardin Khorasan Razavi mai kula da harkokin tsaro da gudanarwa, a gefen taron manema labarai na bayyana fagege da manufofin shirye-shiryen "Babban taron masu hazaka na Hankalin Kasa ga Iran", a cikin hirarsa da manema labarai, ya sanar: Dangane da qudirin kasa, duk wani bayani game da jana'iza da binne Jagoran Shahidi, zata fita ne daga ofishin kiyayewa da yada ayyukan Babban Ayatullahil Uzma Khamene'I Qs ne.
Amerullah Shamqadari ya kara da cewa: An yanke shawara gaba daya don gudanar da jana'izar, amma lokaci da cikakkun bayanai na wannan jana'izar, ta ofishin kiyayewa da yada ayyukan Jagoran Shahidi ne kawai za a fitar da su, wanda zai fara daga Tehran.
Mataimakin gwamnan lardin Khorasan Razavi ya ce: Dangane da qudirin kasar, duk wani bayani game da wannan batu, zai fito ne daga wannan ofishin ne kawai, kuma sauran hukumomi su guji bayar da cikakkun bayanai da kansu.
Shamqadari ya kuma yi nuni da abubuwan da za a yi la'akari da su wajen gudanar da wannan jana'izar, ya kara da cewa: A cikin tsara shirye-shiryen, an yi ƙoƙari samar da saukakawa da amincin jama'a su kasance batutuwa na farko, kuma a kauce wa cunkoso ko kuma faruwar wasu illoli. Hanyoyin da aka keɓe don gudanar da jana'izar ma su dacewa da za a iya bin su.
Ya ce: Idan akwai wasu cikas a hanyar da za a zaba ta ƙarshe, karamar hukumar Mashad ce ke da alhakin kawar da cikas da sassauta hanya.
………………………………………………
Your Comment